Majalisar dattawa ta amince da yancin gashin kan harkokin kudi ga Kananan Hukumomi, majalisun Jihohi, da bangaren shari’a

Date:

Daga Khadija Abdullahi Umar
 A ranar Talata ne majalisar dattawa ta kada kuri’ar yin gyare-gyare ga kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999 wanda ya baiwa majalisun jihohi da na shari’a da kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kansu a fannin kudi.
 A kuri’ar da aka kada a zauren majalisar, ‘yan majalisar dattawa 83 ne suka kada kuri’ar amincewa da ‘yancin cin gashin kan harkokin kudi ga majalisun dokoki da na shari’a na Kananan Hukumomin, yayin da Sanata daya ya ki amincewa da hakan.
 Sanatoci 92 ne suka kada kuri’ar amincewa da kudurin yin gyaran fuska ga ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomin, yayin da Sanatoci biyu suka ki amincewa.
 Majalisar ta yi watsi da shirin sauya sunan karamar hukumar Barkin Ladi da ke jihar Filato zuwa Gwul.
 A kuri’ar da aka kada, ‘yan majalisar dattawa 67 ne suka kada kuri’ar neman sauya suna, yayin da 28 suka ki amincewa.
 Shawarar ta gaza cika kaso biyu bisa ukun da ake bukata.
 Kafin Amincewa da kowane kudiri , dole ne ya samu rinjaye na kashi biyu bisa uku a zauren majalisar dattawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...