Da dumi-dumi: Kwankwaso na shirin ficewa daga PDP zuwa NNPP

Date:

Daga Sayyadi Abubakar

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, na shirin sake ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP.

Tuni dai Sanata Kwankwaso a ranar Talata ya gana da shugabannin jam’iyyar NNPP a wani yunkuri na kammala zuwansa jam’iyyar da ake sa ran zai yi amfani da shi wajen neman takarar shugaban kasa.

Sakataren jam’iyyar na kasa mai barin gado, Ambasada Agbo Gilbert Major ne ya bayyana hakan a Abuja, a wajen taron kwamitin zartarwar ta na kasa (NEC).

Ya ce taron na da nufin daukar muhimman shawarwari da za su mayar da jam’iyyar gabanin babban zaben 2023.

A cewarsa, nan da ‘yan kwanaki gwamnan jihar Kano da ya yi sau biyu zai koma jam’iyyar tare da abokansa.

Ya kuma yi watsi da ba Kwankwaso tikitin takarar shugaban kasa kai tsaye, inda ya ce za a bai wa sauran masu son tsayawa takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...