Da dumi-dumi: Kwankwaso na shirin ficewa daga PDP zuwa NNPP

Date:

Daga Sayyadi Abubakar

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, na shirin sake ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP.

Tuni dai Sanata Kwankwaso a ranar Talata ya gana da shugabannin jam’iyyar NNPP a wani yunkuri na kammala zuwansa jam’iyyar da ake sa ran zai yi amfani da shi wajen neman takarar shugaban kasa.

Sakataren jam’iyyar na kasa mai barin gado, Ambasada Agbo Gilbert Major ne ya bayyana hakan a Abuja, a wajen taron kwamitin zartarwar ta na kasa (NEC).

Ya ce taron na da nufin daukar muhimman shawarwari da za su mayar da jam’iyyar gabanin babban zaben 2023.

A cewarsa, nan da ‘yan kwanaki gwamnan jihar Kano da ya yi sau biyu zai koma jam’iyyar tare da abokansa.

Ya kuma yi watsi da ba Kwankwaso tikitin takarar shugaban kasa kai tsaye, inda ya ce za a bai wa sauran masu son tsayawa takara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...