Da dumi-dumi: Buhari zai tafi Ingila domin duba Lafiyar sa

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara
Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tafi kasar Birtaniya domin duba lafiyarsa wanda ake sa ran zai dauki tsawon kwanaki goma sha hudu.
 Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasar, shi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da yasa Mata hannu a ranar Talata, Inda ya ce shugaban zai halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a Kenya Gabanin ya wuce kasar ta burtaniya.
 Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Adesina ya bayyana cewa shugaban kasar zai bar Abuja ranar Talata 1 ga watan Maris domin halartar bikin cika shekaru 50 da kafa Hukumar Kula da Muhalli ta Majalisar Dinkin Duniya (UNEP@50), wanda aka shirya gudanarwa tsakanin 3 – 4 ga Maris, 2022 a Nairobi, Kenya, don girmama gayyatar da takwaransa na Kenya Uhuru Kenyatta ya yi masa.
 Adesina ya ce Shugaba Buhari zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, Karamin Ministan Muhalli, Sharon Ikeazor, Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Maj.Gen Babagana Monguno (rtd), Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa  Hukumar, Amb. Ahmed Rufai Abubakar, da Shugabar Hukumar ‘Yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...