Mahaifiyar Limamin Masallacin Al-Furqan, Dakta Bashir Aliyu ta rasu

Date:

 

Mahaifiyar fitaccen Malamin addinin musuluncin nan na Jihar Kano, Dakta Bashir Aliyu Umar ta rasu.

Marigayiyar, mai suna Hajiya Khadija Aliyu Harazumi ta rasu da safiyar yau Talata a gidanta da ke Gwale Gudundi bayan ta yi rashin lafiya.

Hajiya Kahdija daya ce daga cikin matan Dan Amar Kano Alhaji Aliyu Harazumi Umar.

Ta rasu ta bar ƴaƴa da jikoki da dama.

Daga ciki akwai babban limamin masallacin juma’a na Al-Furqan da ke unguwar Nasarawa a birnin Kano Dr Bashir Aliyu Umar

Haka kuma za a yi jana’izarta a Kofar Kudu da ke gidan Sarkin Kano da misalin ƙarfe 3 na yamma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: An zabi sabon shugaban jami’ar Bayero BUK

Daga Rahama Umar kwaru   Farfesa Haruna Musa ya zama sabon...

An sake sauya lokacin jana’izzar Aminu Ɗantata – Gwamnatin Nigeria

Gwamnatin tarayyar Nigeria ta ce Hukumomi a Kasar Saudiyyar...

Fadan daba: ku fito ku Kare Kan ku da iyayenku – Gwamnatin Kano ga matasa

Ku tashi ku Kare kanku da iyayen Gwamnatin jihar kano...