Da dumi-dumi: Buhari zai tafi Ingila domin duba Lafiyar sa

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara
Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tafi kasar Birtaniya domin duba lafiyarsa wanda ake sa ran zai dauki tsawon kwanaki goma sha hudu.
 Femi Adesina, mai magana da yawun shugaban kasar, shi ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da yasa Mata hannu a ranar Talata, Inda ya ce shugaban zai halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a Kenya Gabanin ya wuce kasar ta burtaniya.
 Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Adesina ya bayyana cewa shugaban kasar zai bar Abuja ranar Talata 1 ga watan Maris domin halartar bikin cika shekaru 50 da kafa Hukumar Kula da Muhalli ta Majalisar Dinkin Duniya (UNEP@50), wanda aka shirya gudanarwa tsakanin 3 – 4 ga Maris, 2022 a Nairobi, Kenya, don girmama gayyatar da takwaransa na Kenya Uhuru Kenyatta ya yi masa.
 Adesina ya ce Shugaba Buhari zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, Karamin Ministan Muhalli, Sharon Ikeazor, Mai ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Maj.Gen Babagana Monguno (rtd), Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa  Hukumar, Amb. Ahmed Rufai Abubakar, da Shugabar Hukumar ‘Yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...