SADAQATUL JARIYA :Makarantar Islamiyya Na Neman Tallafin a Siya mata Matsuguni

Date:

Daga Abdullahi kano

Makarantar Islammiya ta Madrasatu Zubairu Bin Awwam Litahfizil Qur’an Waddarasatil Islamiyya da ke Unguwar Tunga a karamar hukumar Gwale na neman gudun muwar Bayin Allah domin a siya mata wani kango a unguwar don yin matsuguninta na din din din.

Shugaban Makarantar Malam Abdulrazak Zubairu(Malam Baffa) ne ya bayyana hakan lokacin da yake jawabi yayin bikin saukar Dalibai Goma, wanda makarantar islamiyyar ta gudanar a unguwar Tunga , karamar Hukumar Gwale Kano.

 

Yace makarantar ta sami Albarkar dalibai , inda a kullum dalibai sai karuwa suke sai dai rashin wadataccen Muhalli na kawo tarnaki a fannin cigaban da koyar da dalibai ilmin addinin musulunci.

 

“Muna amfani da wani gida , da kuma kofar gidajen alumma a matsayin ajujuwa to lokacin damina da sanyi muna fuskantar kalubale, wasu magada sun bamu aron kangonsu muna koyar da dalibai a ciki, amma yanzu suna bukatar za su siyar, akan kudi Naira miliyan daya da Rabi.”

 

” Muna rokon Bayan Allah wadanda Allah ya horewa , a taimaka a siya mana wannan kangon, domin wata kungiya tayi mana alkawarin indai mun mallaki filin, za su gina mana ajujuwa fi sabi lillah” inji malam Baffa.

Ga duk Mai bukatar taimakawa zai iya tuntubar malam baffa ,  Tunga a kan wadannan lambobi +234 813 660 8606

Yayin bikin saukar karatun Alqur’ani mai girma na dalibai goma, an gudanar da jawabai na Jan hankali da nasihohi don samar da alumma ta Gari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...