M Pulanis Gombe ya saki Sabon kundinsa Mai Suna Fulbe Duniya

Date:

Daga Zara Jamil Isa

 

Shahararren mawakin fulani nan, Ibrahim Abubakar wanda aka fi sani da M Pulanis Gombe ya fitar da sabon album dinsa mai suna Fulfulde Duuniya.

A cikin wata sanarwa da ya aikowa Kadaura24, tauraron Fulanin ya bayyana cewa sabon Album ɗin nasa za’a iya samunsa tare da sauke shi Kafafen sadarwa na yanar gizo.

Yace a Cikin faifan bidiyon ya baje kolin kyawawan al’adun Fulani a Afirka Wanda Zai kayatar da duk Wanda ya kalle shi, Sannan Kuma yayi Amfani da Kayan daukar sauti da daukar hoto na Zamani irin Waɗanda ake yayinsu a Duniya.

M Pulanis ya kara da cewa sabon kundi “yana zuwa ne bayan kabilar ‘Fulfulde/Pular tana fuskantar babban koma baya”.

M Pulanis Gombe dan asalin jihar Gombe ne a Arewacin Najeriya.

Gwamnatoci kasashe da yawa suna Amfani da harshen Fulatancin a Matsayin harshen kasa, kasashen sun hadar da Senegal, Guinea, Senegambia, Maasina (Nijar Delta ta ciki), Arewa maso Gabashin Najeriya, Kamaru, Mali, Burkina Faso, Gambia, Ghana ta Arewa, Kudancin Nijar da Arewacin Benin (a yankin Borgou, da harshen gida a yawancin kasashen Afirka, irin su Mauritania, Guinea-Bissau, Saliyo, Togo CAR, Chadi, Sudan, Somalia da Habasha, Akwai Mutane sama da miliyan 95 da magana da harshen Fulatanci a duniya.

A Najeriya ana amfani da yare a ko’ina, musamman a yankin Arewa, anfi Amfani da harshen a jihohin da aka Adamawa, Taraba, Bauchi, Gombe, Kano da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...