‘Yan Majalisar Dokokin Zamfara 18 Cikin 22 sun amince da tsige mataimakin gwamnan jihar

Date:

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara da ke arewacin Najeriya ta jefa uria’r amincewa da tsige Mataimakin Gwamnan Mahdi Aliyu Gusau daga kan muƙaminsa da gagarumin rinjaye.

Yayin wani zama a jiya Alhamis, ‘yan majalisa 18 cikin 22 ne suka amince da ɗaukar matakin yayin da ɗaya tak ya ki amincewa.

Haka nan, ‘yan majalisar sun nemi Alƙalin Alƙalai na Zamfara Mai Shari’a Kulu Aliyu ya kafa kwamatin da zai binciki Mahdi bisa zargin saɓa sashe na 190 da 193 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

Dangantaka tsakanin mataimakin gwamnan da uban gidansa Gwamna Bello Muhammad Matawalle ta yi tsami tun lokacin ya gwamnan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC a bara amma Mahdi ya ci gaba da zama a PDP.

Honorabul Shamsudden Hassan Bosko, shi ne Shugaban Kwamitin yada Labarai na majalisar kuma ya shaida wa Haruna Shehu Tangaza yadda aka yi wannan zaman.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...