Ganduje zai kafa Kwamitin da zai tattara tarihin sabbin Masarautun Kano

Date:

Daga Sayyadi Abubakar

 

Gwamnatin Jihar Kano ta ce zata kafa wani Kwamiti na masana da zai tattara tarihin sabbin Masarautun da aka dawo da martabarsu, domin alkinta tarihin don Amfanin al’umma.

Kadaura24 ta rawaito Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan yayin da ya ziyarci Fadar Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya a Juma’ar nan.
Gwamna Ganduje yace Samar da tarihin Masarautun zai sa Sauran al’ummar duniya su san Cewa Masarautun Suna da tarihin da ya kamata a girmama su saboda shi.
Ya bukaci Sarkin na Gaya daya Fara tattara duk abun da ya Sani game da tarihin Masarautar ta Gaya, domin nan gaba kadan za a kafa Kwamitin tare da Kaddamar da shi domin fara aikinsa.
Gwamna Ganduje ya bada tabbacin Gwamnatin Kano zata cigaba da Kai aiyukan Raya Kasa da cigaban al’umma Masarautar ta Gaya domin Cika burin Gwamnatin na Samar da Kananan burane a Jihar Kano.
Gwamna na Kano ya kuma roki al’ummar sabbin Masarautun da su Maida hankali wajen tallafawa yunkurin Gwamnati na bunkasa Masarautun, ta yadda Masu ikirarin zasu rushe Masarautun baza su iyaba ko da sun Sami dama.
A yake nasa Jawabin Mai Martaba Sarkin Gaya Alhaji Aliyu Ibrahim Gaya ya yabawa Gwamna Ganduje bisa aiyukan Raya Kasa da cigaban al’umma a Masarautar ta Gaya don Kara inganta ta.
Mai Martaba Sarkin ya Kuma ce ita ma Masarautar tana nata kokarin wajen Ganin an Samar da tituna futilun hanya da Sauran abubuwan da zasu Kara bunkasa Masarautar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...