Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman
Shahararriyar yar wasan Hausa nan wacce take fitowa a matsayin uwa ko kaka a masana’antar Kanywood Ladin Cima Haruna ta koka game da yadda ake biyanta kudin Aikin da take yi na fitowa a Fina-finan Hausa.
Kadaura24 ta rawaito Ladin Cima ta bayyana koken nata ne Cikin Wata Hira da suka yi da Sashin Hausa na BBC a cikin Shirin su na “Daga Bakin Mai ita” Wanda a Cikin sa suke tattaunawa da Yan wasan Hausa.
Dattijiwar Wacce ta ce ta kwashe sama da Shekaru 50 tana harkar fim, tace taba shiga Matsalar da ko Yanzu ta tuna ta sai tayi kuka wato Matsalar Rashin muhalli.
“Banda Allah ya tsare da yanzu ina bakin bata ina kwana sakamakon matsalar da na shi ga, Amma Allah ya rufamin asiri na fadawa Mutane shi ne Allah ya taimakeni na fita daga cikin Matsalar”.inji Ladin cima
Bayan an tambayi Ladin cima ko ya akai bata tara abun da ta ke samu ba don mallakar Muhallin, sai ta kada baki tace ai ba Wani abun Mai yawa ake bani in nayi fim din ba.
” Ban taba yin Fim an bani Naira dubu 50 ko 30 ko ma 20 ba, Naira duba 5 ce ko 3, yauma na je nayi Aiki Naira duba 2 aka bani to me naci me na ajiye a dubu 2 ko 3?.”
Tace akwai ‘ya’ya 7 da ita take kula da su don haka tace bata da ikon adana Wani abun a Dan abun da ake bata .