ASUU ta ce ta yanke Kauna da Gwamnatin Buhari

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara

 

Kungiyar malama jami’a ta Najeriya ASUU ta nuna shakkunta game da cika alkawuran da gwamnatin shugaba Buhari ta dauka na samar da mafita ga matsalolin da fannin ilimin kasar ke ciki, musammam jami’u.

Kungiyar ta ce za ta fara yajin aikin sai baba ta gani nan ba da jimawa ba.

Kungiyar ta bayyana lamarin da ke faruwa a halin yazu da “abin kunya” yadda gwamnatin tarayya ke ci gaba da kare tsarin biyan kudi na IPPIS duk da zargin cewa akwai almundahana a cikinsa, kamar yadda ya bayyana a cikin rahoton da babban akantan tarayyar Najeriya ya gabatar a gaban Majalisar dattawan kasar.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, ASUU ta nuna fushinta kan yadda aka rika zaman sasanci tsakaninta da gwamnati kan yadda za a farfado da ilimi sai dai gwamnati ta gaza dabbaka abin da take ta ikirari a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...