SERAP ta kai karar Buhari kotu kan batan Naira biliyan 3

Date:

Daga Halima M Sadeeq

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci a Najeriya ta shigar da karar Shugaba Buhari gaban kotu “kan gaza gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan kudaden da suka kai naira biliyan 3 daga ma’aikatar kuɗi ta kasar, domin tabbatar da an gurfanar da wadanda ake zargi da hannu ciki da kuma kwato kudaden.”

Karar ta biyo bayan batan dabon da ake zargin da ofishin babban akanta janar na kasar ya shigar a 2018 da 2019 na rahoton da yake fitarwa, wanda aka batar da su ba bisa ka’ida ba ko kuma ba a bayar da bayanansu ba.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP a Jihar Kano

BBC Hausa ta rawaito karar mai lamba FHC/L/CS/148/22 an shigar da ita ne a ranar Juma’ar da ta gabata a wata babbar kotun Tarayya da ke Lagos, kamar yadda SERAP ta bukata:

“umarnin da zai sanya Shugaba Buhari ya tabbatar da an gudanar da bincike game da zargin da ake yi na batan naira biliyan 3.1 wadanda kudaden mutanen Najeriya ne, a gabatar da duk wanda ake zargi gaban kotu, kuma a kwato kudaden al’umma.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...