Kasar cameroon da Burkina faso sun kai ga zagayen wasa na kusa dana karshe a gasar 2021 AFCON

Date:

Zaharadeen saleh

Mai masaukin baki kasar kamaru ta samu nasarar kaiwa ga zagayen wasa na kusa dana karshe a gasar cin kofin kwallon kafa ta kasashen nahiyar Afrika karo na 33 wadda ake gudanarwa yanzu a kasar kamaru.

KADAURA24 ta rawaito Kasar kamaru takai ga zagayen wasan na kusa dana karshen ne bayan data samu nasarar doke kasar Gambia da ci biyu da nema a zagayen wasa na daf dana kusa dana karshe da suka fafata a ranar asabar din nan.

Dan wasan kasar ta kamaru mai suna Toko Ekambi ya samu nasarar jefa kwallo guda biyu araga a mintina 50 da kuma 57.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP

Haka zalika itama kasar Burkina Faso ta samu nasarar doke kasar Tunisia daci daya da nema ta hannu dan wasanta mai suna Ouattara daya jefa kwallo daya tilo araga ana daf da tafiya hutun rabin lokaci.

A yammacin ranar Lahadin nan ce za’a fafata ragowa wasanin guda biyu na zagayen wasa na daf dana kusa dana karshe a tsakanin kasar Masar da kasar Morocco da misalin karfe biyar na yamma, sai kuma kasar Senegal zata kara wasa da kasar E/ Guinea da misalin karfe takwas na dare agogon Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...