Kasar cameroon da Burkina faso sun kai ga zagayen wasa na kusa dana karshe a gasar 2021 AFCON

Date:

Zaharadeen saleh

Mai masaukin baki kasar kamaru ta samu nasarar kaiwa ga zagayen wasa na kusa dana karshe a gasar cin kofin kwallon kafa ta kasashen nahiyar Afrika karo na 33 wadda ake gudanarwa yanzu a kasar kamaru.

KADAURA24 ta rawaito Kasar kamaru takai ga zagayen wasan na kusa dana karshen ne bayan data samu nasarar doke kasar Gambia da ci biyu da nema a zagayen wasa na daf dana kusa dana karshe da suka fafata a ranar asabar din nan.

Dan wasan kasar ta kamaru mai suna Toko Ekambi ya samu nasarar jefa kwallo guda biyu araga a mintina 50 da kuma 57.

Sakon taya Murnar Samun shugabancin jam’iyyar SDP

Haka zalika itama kasar Burkina Faso ta samu nasarar doke kasar Tunisia daci daya da nema ta hannu dan wasanta mai suna Ouattara daya jefa kwallo daya tilo araga ana daf da tafiya hutun rabin lokaci.

A yammacin ranar Lahadin nan ce za’a fafata ragowa wasanin guda biyu na zagayen wasa na daf dana kusa dana karshe a tsakanin kasar Masar da kasar Morocco da misalin karfe biyar na yamma, sai kuma kasar Senegal zata kara wasa da kasar E/ Guinea da misalin karfe takwas na dare agogon Nigeria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

NAHCON ta sanar da ranar da za a fara jigilar Maniyatan Nigeria zuwa kasar Saudiyya

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar kula da aikin hajji ta...

Hisbah ta rushe wajen da aka ce sawun Ma’aiki ya fito a jihar Kano

    Hukumar Hisbah ta kai samame tare da rushe wani...

ƴan siyasa ne su ka kashe Arewacin Nigeria — Inji Gwamna Uba Sani

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa ‘yan...

Shugaban Karamar hukumar Bagwai ya kaddamar da aikn gada ta sama da Naira Miliyan 160

Daga Shu'aibu Sani Bagwai   Karamar hukumar Bagwai a jihar Kano...