Tallafawa Ilimi : Falakin Shinkafi ya Zama Gwarzon Shekara – S M S

Date:

Daga Zubaida Abubakar Ahmad

Kungiyar Tsofaffi Daliban Kwalejin Kimiyya da fasaha ta Jihar Kano bangaren Waɗanda suka karanci Ilimin Gudanar Wato ( school of management studies alumni) ta Karrama Ambassador Yunusa Yusuf Hamza (Falakin Shinkafi) da Lambar yabon mafi girma.

KADAURA24 ta rawaito an Gudanar da taron Karramawar ne a Ranar asabar din nan.

Shugabannin Kungiyar sun ce sun Karrama Falakin Shinkafi ne Sakamakon irin Gudunmawar da ya ke baiwa Ɗalibai don tallafa musu.

Ambassador Yunusa ya kasance a Koda yaushe baya gajiyawa wajen taimakawa dalibai domin su Sami damar samun Ilimi nagartacce ,ko Kuma taimakawa makarantu”.

“Mun baiwa Falakin Shinkafi Lambar yabo ne ta Mai tallafawa don cigaban Ilimi”.

Da yake Jawabi a wajen taron Ambassador Yunusa Yusuf Hamza (Falakin Shinkafi) ya godewa’ya’yan Kungiyar bisa Karramawar da sukai Masa Cikin dubban Mutanen da suke Kasar nan.

Wannan Lambar yabon Babu shakka zata karamin kwarin gwiwar cigaba da bada Gudunmawa don cigaban Ilimi”. Falaki

Yace ya Zama wajibi a tallafawa al’umma Musamman Matasa don su Sami ingantaccen Ilimi na addini da na boko, don cigaba al’umma.

Ina Kira ga mawadata da Shugabanni a kowanne mataki da su Rika tallafawa Matasa don su Sami Ilimi Mai inganci Wanda za a yi alfahari da su a nan gaba, kamar yadda kullum ake cewa Yara Manyan gobe”. Inji Falakin Shinkafi

Taron dai ya Sami halartar Al’umma da dama daga Ciki da wajen jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...