Hadimin Ganduje SSA Gwarmai ya sake rabawa matasa kudi, Mashina da Jakai don inganta Rayuwarsu

Date:

Daga Sayyeed Abubakar

 

Mataimaki na musamman ga Gwamna jihar kano a kan harkokin matasa Alhaji Murtala Gwarmai ya rabawa matasa guda shida babura domin saukaka musu a sha’anin sufuri a wani yunkuri na basu damar sharbar romon damakaradiyya.

Da yake zantawa da manema labarai Alhaji Murtala Gwarmai yace ya rabawa matasa babura da jakunan ne domin cika umarnin gwamnan kano Abdullahi Umar Ganduje na tallafawa mata da matasa don inganta rayuwarsu kamar yadda yake yi a matakin jihar.

Gwarmai yace ya zama wajibi ya bada tallafin saboda irin gudunmawar da suka baiwa gwamnatin kano musamman a zaben shekara ta 2019 da ya gabata, da kuma kokarin da suke yi na ganin sun dogara da kawunansu.

A yau mun bada babura guda shida ga matasa sannan daya daga cikinsu yace shi jakai yake bukata domin inganta harkokinsa na Neman abinchi wanda yake gudanarwa don ya rufawa Kansa asiri”. Inji Gwarmai.

Bayan ya rabon baburan Hadimin na Ganduje ya baiwa wasu matasa 4 tallafin naira dubu Dari biyu da hamsin kowannensu tare kuma da mikawa wata mata takardar shidar daukar aiki a ma’aikatar lafiya ta jihar kano.

ina so Ku sani na baku waɗanan babura da kudin ne saboda ku ma Ku sharbi romon damakaradiyya, kuma Mai gidanmu Hon. Murtala Sule Garo ya taka rawa sosai wajen tabbatuwar wannan al’amari don haka idan kuka gidewa Gwamna Ganduje to Ku godewa Hon. Murtala Sule Garo sannan kuma Nima sai ku rabani cikin godiyar”.
Inji SSA Gwarmai

Mai kudi meku da Muhd sani sabalanga na daga cikin wadanda suka amfana da tallafin na wannan lokaci sun godewa Hon Murtala Sule Garo da Hon. Murtala Gwarmai bisa abun alkhairin da S SA din yayi musu, tare kuma da bada tabbacin yin amfani da tallafin ta hanyar data dace.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...