‘Yar Shehu Ibrahim Inyass ta shiryawa Nigeria addu’o’in samun zaman lafiya a kano

Date:

SAMINU IBRAHIM MAGASHI
Sayyada Rahmatullah sheikh Ibrahim Inyas ta jagoranci karantun dala’ilu tare kuma da yiwa masa addu’a domin samun dauwamammen zaman lafiya a Nigeria.
Kadaura24 ta rawaito cewa Sayydarar ta bayyana cewa babban makasudin da yasa suka kira maulidin na bana dana yiwa Kasa addu’a shi ne saboda da irin yanayin da Kasar nan suka ta fada na tabarbarewa tsaro da tashe tashen hankulan al’umma Nigeria.
An dai gudanar taron addu’o’in da saukar dala’ilu ne a masallacin juma’a na Sheikh Ibrahim Inyass dake unguwar Gadon kaya a birnin kanon dabo.
 ” Matsalolin tsaron da kasar nan take fuskanta akwai bukatar al’umma a kungiyance ko a daidaiku a rika yin addu’ar Allah ya kawowa Nigeria saukin matsalolin tsaro da suka addabi al’umma”.
Inji Sayyada Rahmatullah
Shi ma a jawabinsa khalifan tijjaniya na kasa Muhd Sanusi II Wanda yasamu wakilcin Alhaji Mujittafa Falaki  ya yiwa daukacin al’umma fatan alkhairi tare da Jan hankalin matasa wajan ganin sunbtashi haikan wajen neman nakansu kasancewar ita ce hanya daya tilo da zata kawo cikakken tsaro a kasar nan.
Ya yabawa wadanda suka shirya taron tare kuma da fatan mutane zasu gyara tsakaninsu da Allah ko a sami saukin matsalolin da suka addabi al’umma.
taron dai ya sami halartar dumbin al’umma na ciki da wajan kasarnan ciki kuwa harda Yaya” da jikokin Shehu Ibrahim Inyass da kuma halifofin tijjaniyya da mukaddamai da muridai da dai sauran manya baki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...