‘Yar Shehu Ibrahim Inyass ta shiryawa Nigeria addu’o’in samun zaman lafiya a kano

Date:

SAMINU IBRAHIM MAGASHI
Sayyada Rahmatullah sheikh Ibrahim Inyas ta jagoranci karantun dala’ilu tare kuma da yiwa masa addu’a domin samun dauwamammen zaman lafiya a Nigeria.
Kadaura24 ta rawaito cewa Sayydarar ta bayyana cewa babban makasudin da yasa suka kira maulidin na bana dana yiwa Kasa addu’a shi ne saboda da irin yanayin da Kasar nan suka ta fada na tabarbarewa tsaro da tashe tashen hankulan al’umma Nigeria.
An dai gudanar taron addu’o’in da saukar dala’ilu ne a masallacin juma’a na Sheikh Ibrahim Inyass dake unguwar Gadon kaya a birnin kanon dabo.
 ” Matsalolin tsaron da kasar nan take fuskanta akwai bukatar al’umma a kungiyance ko a daidaiku a rika yin addu’ar Allah ya kawowa Nigeria saukin matsalolin tsaro da suka addabi al’umma”.
Inji Sayyada Rahmatullah
Shi ma a jawabinsa khalifan tijjaniya na kasa Muhd Sanusi II Wanda yasamu wakilcin Alhaji Mujittafa Falaki  ya yiwa daukacin al’umma fatan alkhairi tare da Jan hankalin matasa wajan ganin sunbtashi haikan wajen neman nakansu kasancewar ita ce hanya daya tilo da zata kawo cikakken tsaro a kasar nan.
Ya yabawa wadanda suka shirya taron tare kuma da fatan mutane zasu gyara tsakaninsu da Allah ko a sami saukin matsalolin da suka addabi al’umma.
taron dai ya sami halartar dumbin al’umma na ciki da wajan kasarnan ciki kuwa harda Yaya” da jikokin Shehu Ibrahim Inyass da kuma halifofin tijjaniyya da mukaddamai da muridai da dai sauran manya baki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...