Gwamnatin Tarayya ta Janye haramcin da ta saka wa Twitter

Date:

Daga Muzammil sani yola

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya janye haramcin da ya saka wa Twitter a ƙasar.

Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya tabbatar wa BBC da hakan.

Ana sa ran daga 13 ga watan Janairun 2022 matakin na gwamnatin ƙasar zai soma aiki.

Tun a watan Yunin 2021 ne gwamnatin Najeriya ta haramta amfani da Twitter a ƙasar bayan ta yi zargin cewa ana amfani da shafin wajen kokarin tarwatsa kasar ta hanyar yada labaran karya da ke iya haddasa ”tashe-tashen hankula”.

Hakan ya haifar da martani mai zafi daga ‘yan Najeriya da dama da suke kallon matakin a matsayin taka hakkin bila dama, amma kuma gwamnati ba ta nuna wata damuwa ba, inda ta bar shafin na Twitter a kasar ya ci gaba da kasancewa a toshe.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...