Da dumi-dumi : Yan adaidaita Sahu sun janye yajin aikin da suka tsunduma

Date:

Daga Aminu Abba

 

Gamayyar ‘yan adaidaita Sahu a jihar kano sun janye yajin aikin da suka tsunduma tun ranar litinin din data gabata sakamakon wani zama da akai da bangarensu da na gwamnati karkashin jagorancin Shugaban Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano Barr. Mahmoud Gadanya.

 

Kadaura24 ta rawaito Barr. Abba Hikima dai shi ne ya wakilci bangaren yan adaidaita Sahun,yayin da Shugaban hukumar karota Baffa babba Dan agundi ya wakilci gwamnatin jihar kano.

 

Yayin zaman an cimma matsaya kamar haka:

1. Za a rubutawa gwamnatin jihar kano takardar Neman ragin kudin sabunta rigistar na naira dubu 8.

2. Yan adaidaita Sahu za su dawo aiki a gobe alhamis.

3 . za a jira gwamnatin ta tsaida matsaya kafin ranar 18 ga wannna wata da za a sake zama.

4 . Yan adaidaita Sahu za su cigaba da biyan Naira 100 harajin kullum-kullum.

Wadannan dai Su ne abun da aka cimma yayin zaman da aka gudanar a yau a ofishin Kungiyar lauyoyi ta kasa reshen jihar Kano, kuma yayin zaman kowanne bangare ya aminta da duk abubuwan da aka cimma.

1 COMMENT

  1. Hello there! This is my first comment here so I just wanted to
    give a quick shout out and say I really enjoy reading through your blog posts.
    Can you suggest any other blogs/websites/forums that cover
    the same topics? Thank you!

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...