Gwamnatin Tarayya ta Janye haramcin da ta saka wa Twitter

Date:

Daga Muzammil sani yola

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya janye haramcin da ya saka wa Twitter a ƙasar.

Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya tabbatar wa BBC da hakan.

Ana sa ran daga 13 ga watan Janairun 2022 matakin na gwamnatin ƙasar zai soma aiki.

Tun a watan Yunin 2021 ne gwamnatin Najeriya ta haramta amfani da Twitter a ƙasar bayan ta yi zargin cewa ana amfani da shafin wajen kokarin tarwatsa kasar ta hanyar yada labaran karya da ke iya haddasa ”tashe-tashen hankula”.

Hakan ya haifar da martani mai zafi daga ‘yan Najeriya da dama da suke kallon matakin a matsayin taka hakkin bila dama, amma kuma gwamnati ba ta nuna wata damuwa ba, inda ta bar shafin na Twitter a kasar ya ci gaba da kasancewa a toshe.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...