Wani Yaro Dan Shekaru 4 Rasu Bayan ya fada Rijiya a Kano

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani yaro mai shekaru hudu Mai Suna Mustapha Dalhatu a Kofar Dawanau dake karamar hukumar Ungoggo a jihar.
 Jami’in hulda da jama’a na hukumar SFS Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatarwa manema labarai faruwar lamarin a kano.
 Ya bayyana cewa hukumar ta samu kiran ceto daga wani Aminu Sani Shu’aibu cewa wani karamin yaro ya fada cikin rijiya.
 Saminu Yusif ya yi nuni da cewa, da tawagar su ta isa ta yi nasarar ceto yaron Cikin Mawuyacin Halin, inda daga bisani jami’an lafiya suka tabbatar da mutuwarsa.
 Ya ce an mika gawar marigayin ga hakimin unguwar Dawanau, Alhaji Musa Habibu.
 Hakazalika, ‘yan kwana-kwana na jihar Kano sun kashe wata gobara da ta tashi a layin ‘Yan Robobi da ke Kasuwar Kofar Wambai a karamar hukumar Kano.
 Da yake bayyana lamarin kakakin hukumar ya ci gaba da cewa shago daya gobarar ta shafa.
 Ya ce babu wani rai da aka rasa a lokacin faruwar lamarin, sakamakon daukin gaggawar da hukumar kashe gobara ta Kano ta Kai Wajen.
 Jami’in hulda da jama’a ya bukaci jama’a da su tabbatar da daukar matakan hana Faruwar gobara a kowanni lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...