Shugaban Majalisar Wakilai ya Dauki Nauyin Karatun Dalibai 130 a Kano

Date:

Daga Kabiru Muhd Getso

 

Kungiyar Ma’aikatan Ofishin Shugaban majalisar wakilai Femi Gberjabiamila (Gbaja Professinals Volunteers Network ) da hadin kwiwar Kungiyar Malaman gaba da sakandire ta yankin Dawakin Tofa sun Dauki Nation Karatun daliban yankin har su 130 tun daga matakin firamare.

 

Kadaura24 ta rawaito Shugaban ma’aikatan ofishin Shugaban majalisar Hon Sunusi Garba Rikiji wanda ya wakilci Shugaban majalisar ya bayyana cewar wannan tsari somin ta6i ne, domin zasu cigaba da aiwatar dashi a sassa daban-daban dake fadin kasarnan.

 

Ya kara da cewar Shugaban majalisar kullun zuciyarsa a bayyana take wajen daukar Nigeria a Matsayin dunkulalliyar kasa baki daya, shi yasa kullum yake kokarin aiwatar da shirin tallafawa karatun kananan yara a kowanne yanki a kasar nan.

Daga Cikin Albashin Sa, Shugaban Kano Poly ya sake Rabon Naira Dubu Biyar-Biyar a Dawakin Tofa

Shi ma a nasa jawabin shugaban karamar hukumar Hon Ado Tambai Gwa wanda ya samu wakilcin mataimakinsa Garba Yusif Labour ya nuna farin cikinsa bisa wannan kabakin arziki da karamar hukumar Dawakin Tofa ta samu, inda ya bayyana gamsuwarsu da irin wannan gudummuwa da suka samu, ya Kuma ja hankalin Sauran al’umma masu rike da madafun iko da suyi koyi da wannan kyakkyawan tsari.

 

A karshe Hakimin Dawakin Tofa Alh Isma’il Umar Ganduje ya bayyana jin dadinsa bisa wannan abin alheri tare da fatan A’ummar da suka taru a wajen kaddamarwa sun koma gida lafiya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...