Shekara 2022 Shekara ce ta sulhu da zaman lafiya – Ganduje

Date:

Daga Aisha Mai Agogo
 Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya ce ya kamata sabuwar shekara ta 2022 ta kawo sabon zaman lafiya da sulhu a tsakanin masu ruwa da tsaki a jam’iyyun siyasa a jihar nan da ma kasa baki daya.
 Ya ce ya kamata a ce watanni masu zuwa su zama na dimokuradiyyar cikin gida inda za a  samu ci gaba a jam’iyyun siyasar Jihar nan, yace yi hakan zai samar da wakilai masu nagarta a matakai daban-daban wadanda suke da kwarewa wanda su ci gaba da gina kano kan tsare-tsare da manufofin da shugabannin da suka shude suka assasa.
Kadaura24 ta rawaito a sakon sabuwar shekara ga al’ummar jihar wanda kwamishinan yada labarai na jihar Malam Muhammad Garba ya fitar, gwamnan ya ce daga dukkan alamu abubuwan da suka faru a Kano na iya kawo wani sabon salo a tarihin siyasar jihar.
 Ya ce al’ummar Kano dake da kishin cigaban Kano Sun nuna bukatar ganin Manyan ‘yan siyasar Kano sun yi sulhu da juna, domin ganin an samar da zaman lafiya da ci gaba mai inganci a fagen siyasa da al’amuran cigaban al’umma.
 Sanarwar ta nuna matukar damuwa kan yadda ake ta fama da tabarbarewar tsaro a fadin kasar baya ga fatara da ake fama da ita sakamakon tabarbarewar tattalin arziki a kasar.
 Sai dai ya bayyana fatansa na cewa duk da kalubalen da ake fuskanta gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari na ci gaba da kokarin ganin an aiwatar da manufofinta da shirye-shiryen yadda za a ragewa al’umma radadin talauci.
 Gwamnan ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin sa, wadda kasafin kudin 2022 ya Mai da hankali wajen kammala ayyuka, da kuduri aniyar kyautata wa al’umma ta hanyar kawo sauyi a yankunan karkara da kuma shirye-shiryen karfafa tattalin arzikin Jihar Kano.
 Yayin da yake taya al’ummar kasar murnar shigows sabuwar shekara, Ganduje ya kuma yi kira da a hada kai da yi wa Najeriya addu’a musamman malaman addini su rika wa’azi akan zaman lafiya, hakuri da juna duk da kalubalen da ake fuskanta.

17 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...