Rashin Tsaro: Zabukan Shekara ta 2023 Su na Cikin Hadari – INEC

Date:

Hukumar zaɓen Najeriya INEC ta yi gargaɗin cewa zaɓukan ƙasar na 2023 na iya kasancewa cikin hadari, matukar ba a yi kokarin daƙile matsalar rashin tsaro ba.

A cewar hukumar kalubalen tsaron da ke kara ta’azzara da rashin hukunta masu kawowa shirinta tsaiko ba zai taimaka wajen cimma burinta na yin ingantaccen zabe ba.

BBC Hausa ta rawaito INEC ta ce tun yanzu ta fara tsoron tura ma’aikatan wucin gadi zuwa yankunan da ake fama da rikici, wadanda kuma dole ne a yi zaɓen a cikinsu.

Ta kara da cewa su kansu da yawa daga cikin sama da ma’aikata miliyan daya da ba na dindindin ba da take amfani da su sun nuna fargaba tun yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...