Covid-19: An Daina Hada Sahun Sallah a Masallacin Ka’aba da na Annabi dake Madina

Date:

An dawo da dokar tilasta bayar da tazara da saka takunkumi a Masallacin Ka’aba a Makkah da kuma na Annabi a Madina, kamar yadda hukumomin da ke kula da Masallatan Biyu Masu Daraja na Saudiyya suka bayyana.

Matakin zai fara aiki ne daga ranar Alhamis, inda hukumomin suka ce yanzu saka takunkumi da bayar da tazara ya zama wajibi.

Hukumomin sun ce matakin ya shafi masu aikin Umrah da masu ɗawafi da sauran masu Ibada a masallatan biyu.

Sannan an yi gargaɗi ga baƙi da ma’aikatan Masallatan biyu su mutunta dokar.

Dokokin za su rika aiki a cikin gidaje da kuma waje inda mutane ke mu’amalar yau da kullum.

A ‘yan kwanakin nan masu kamuwa da korona na karuwa a Saudiyya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...