Rahoton Binciken Yadda Shanu ke Jigata Idan an Dauke su Daga Arewa zuwa Kudancin Nigeria

Date:

Daga Sani Abdullahi Danbala Gwarzo

 

Babbobi Musamman Dangin su shanu na fuskantar kalubale ya yin da aka debesu daga jihohin Arewa zuwa kasuwannin kudu Musamman jahar lagas.

Dabbobin na fuskantar Kalubalen ne sakamakon irin yadda suke shan wahala kafin su isa daga arewa zuwa kudu, a mafi yawan lokaci dai akan kai dabbobin ne a tsaye wanda hakan yake sawa wasu ke kasa tashi idan sun zauna wasu kuma ke haduwa da karaya ko gocewar Kashi a takaice dai Suna jigata.
 Wakilin Kadaura24 ya da ya ziyarci wasu kasuwannin shanu a jahar lagas, ya sami jin ta bakin wani matashi mai suna Naziru Ya’u dake tsaka da tashin wata shaniya, inda ya bayyana dalilan dake sabbaba irin jigatar da dabbobin suke yi jkafin zuwan su kudu daga arewa.
Yace Suna jigata ne sakamakon dauri da tsayiwa ga kuma tafiya mai nisa wanda  motar shanun takan iya wuce kwana biyu kafin su karasa Jihar ta Lagos Saboda yanayin Motocin da suke daukar dabbobin.
 “Idan mun sami dabbobin da suka jigata sai dai a dauki kurar shanu a dauko su daga mashigar kwata zuwa mayan domin su dabbobin baza su iya takawa da kafafuwansu ba.” Inji Naziru Ya’u
Matashin yace a wasu lokutan ma akan Sami saniyar da ba zata iya ko da yin fitsari ba Saboda da jigata, Inda yace idan suka Sami Waɗanda Suka galabaita to lashakka sai dai kawai a yanka ta.
Irin Wannan nan Matsaloli da dabbobin suke fuskanta babu shakka zasu iya yiwa naman su lahani, Wanda kuma hakan zai iya saukowa har Mutanen da Suka ci naman.
Akwai bukatar dai bukatar masu gudanar da irin wannan sana’ar, su Rika daukar kwararan matakai Waɗanda zasu rika saukakawa dabbobin su rinka isa kudun Cikin hayyacinsu,watakil ko al’umma sa Sami nama mai kyau wanda zai inganta lafiyar su.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

‎Kawu Sumaila ya binciko kudaden da gwamnatin tarayya ta turawa kananan hukumomin Kano

‎ ‎Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Suleiman Abdulrahman Kawu...

Kamata ya yi wajen Mauludi ya Zama waje Mai nutsuwa saboda ana ambaton Allah da Manzonsa – Mal Ibrahim Khalil

Shugaban Majalisar shuhurar Malamai ta jihar Kano Sheikh Malam...

Ra’ayi:‎Tsarin Kwankwasiyya ya dora Kano a gwadaben cigaba a mulkin Gwamna Abba Kabir -Adamu Shehu Bello

‎ ‎Ra’ayi ‎ ‎Daga Adamu Shehu Bello (Bayero Chedi), Jigo a Kwankwasiyya...