Ma’aikatan Kananan Hukumomi sun yi Mana yawa a Katsina – Gwamna Masari

Date:

Gwamnan Jihar Katsina Aminu Bello Masari ya buƙaci shugabannin ƙaramar hukuma da ake shirin zaɓa a jihar da su dage wajen tara kuɗin shiga domin su biya ma’aikatansu albashi “saboda sun yi yawa”.

Masari ya bayyana haka ne ranar Talata yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Katsina, yana mai cewa “albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi ya yi yawa”.

“Game da kuɗaɗen ƙaramar hukuma, gaskiya ne lokacin da muka zo, kusan dukkansu ma’aikatansu sun yi yawa,” a cewarsa.

“Mun yi ƙoƙarin biyansu hannu da hannu don gano haƙiƙanin yawan adadinsu amma duk da haka ba mu iya rage yawan kuɗin da ake biyan su ba a matakin ƙaramar hukuma. Amma kuma dukkansu suna da shaidar ɗaukar aiki ta gaskiya.”

Gwamnan ya ce gwamnatin da ta gabata ce ta dakatar da albashin ma’aikata 2,000.

14 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...