Zawiyyar Malam Bala Maiyafe ta Shirya taron yiwa Kasar addu’ar Zaman Lafiya

Date:

Daga Saminu Ibrahim Magashi
Zawiyar malam Bala maiyafe dake unguwar adakawa a jihar kano ta hada gangamin taron yiwa kasa addu’oin neman zaman lafiya, yayin da a gefe guda Kuma zawiyar tayi hubbasa wajan ganin ta shiga sahun masu tallafawa marasa karfi da marayu ta hanyar Samar da Gidauniyar.
Yayin taron addu’ar an yi saukar  karatun Ishiriniya, tare da gabatar da makaloli daga bakin malamai da dama, da niyyar jawo hankalin al’umma da kuma kara sanin muhimmancin zaman lafiya da neman ilmin addini da kuma ruko da Zumunci.
Datake bayani Shugabar Gidauniyar Dr Atika Bala Maiyafe, ta bayyan cewa sunyi wannan yunkurine domin zaburar da masu hannu da shuni wajan shirya irin wanann tarurruka domin yiwa qasa addu’a.
Dr. Atika ta kuma kara da cewa lokaci zuwa lokaci za su rika shirya irin Wannan taron addu’ar domin nemawa kasar nan dauwamammen Zaman Lafiya.
Taron dai yasamu halittar dumbin al’umma da suka hada da malam Sheikh Ibrahim Khalil, Sheikh Umar Sani Fagge, da sarkin fawa na jihar kano da dai sauran muhiman mutane.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bayan shekaru 20, Kotun Ƙoli ta sanya ranar yanke hukunci kan rikicin masarautar Gwandu

Kotun Koli ta sanya ranar yanke hukunci kan daukaka...

Hukumar Shari’ah ta kaddamar da kwamatoci domin kawo sauye-sauye game da cigaban Shari’a a jihar Kano

  Hukumar Shari'ah ta jihar Kano karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta...

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...