Ku Daina Hadani da Wasu Gwamnoni a Ƙasar nan – Zulum ya Fadawa Yan Social Media

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya roki masu kwatanta ayyukansa da na sauran gwamnoni su daina.

Zulum ya yi rokon ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Isa Gasau ya fitar ranar Litinin.

BBC Hausa ta rawaito Gwamnan ya yaba wa mutanen da ke tallata ayyukansa a shafukan sada zumunta, sai dai ya ce bai kamata a rika kwatanta “ayyukanna da na sauran gwamnoni ba, tun da dukkan jihohin suna da bambanci”.

“Duk da yake Ina matukar godiya bisa dukkan goyon baya da tallata ayyukana, a kwanakin nan, na samu sakonni, inda ake kwatanta ayyukan da muke yi a Borno da na wasu jihohi, a wasu lokutan ma ana zagi.

Gaskiya ba na jin dadi a duk lokacin da aka kwatanta ni da wani gwamna ta hanyar muzanta shi, musamman idan wadanda suke yin hakan suna cikin masu amfani da shafukan sada zumuntar da ke da alaka da mu”, in ji Gwamna Zulum.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...