Gwamna Ganduje ya nada Ahmad Sulaiman Kwamishina

Date:

Daga Abubakar Na’Allah Kura

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmed Sulaiman kwamishina na biyu a hukumar kula da makarantun firamare ta jihar Kano.

Gwamnan ya mikawa Shehun Malamin takardar shaidar Kama Aiki ne a Gidan Gwamnatin Jihar Kano a gaban Shugaban Kungiyar Izala na Kasa Sheikh Abdullahi Bala Lau da Sakataren sa Sheikh Kabiru Haruna Gombe.

Kadaura24 ta rawaito Gwamnan ya ce ya nada Malam Ahmad Sulaiman Matsayin Kwamishinan na biyu ne Saboda irin Gudunmawar da ya dade yana bayarwa wajen cigaban ilima da harkokin addinin Musulci a Jihar Kano.

Ya Kuma bukace shi ya zamo Mai cigaba da bada Gudunmawar don inganta harkokin Ilimi a Jihar Kano Kamar yadda Gwamnatinsa ta kudiri aniyar yin hakan.

Malam Ahmad Sulaiman ya roƙi Allah ya sa albarka a kujerar da ya samu da kuma roƙon addu’ar jama’a kan taya sa riƙo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...