Gwamna Ganduje ya nada Ahmad Sulaiman Kwamishina

Date:

Daga Abubakar Na’Allah Kura

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya naɗa Alaramma Ahmed Sulaiman kwamishina na biyu a hukumar kula da makarantun firamare ta jihar Kano.

Gwamnan ya mikawa Shehun Malamin takardar shaidar Kama Aiki ne a Gidan Gwamnatin Jihar Kano a gaban Shugaban Kungiyar Izala na Kasa Sheikh Abdullahi Bala Lau da Sakataren sa Sheikh Kabiru Haruna Gombe.

Kadaura24 ta rawaito Gwamnan ya ce ya nada Malam Ahmad Sulaiman Matsayin Kwamishinan na biyu ne Saboda irin Gudunmawar da ya dade yana bayarwa wajen cigaban ilima da harkokin addinin Musulci a Jihar Kano.

Ya Kuma bukace shi ya zamo Mai cigaba da bada Gudunmawar don inganta harkokin Ilimi a Jihar Kano Kamar yadda Gwamnatinsa ta kudiri aniyar yin hakan.

Malam Ahmad Sulaiman ya roƙi Allah ya sa albarka a kujerar da ya samu da kuma roƙon addu’ar jama’a kan taya sa riƙo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ku ba da gudunmawa kano ta zauna Lafiya – Waiya ya shawarci yan jaridun yanar gizo

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci kafafen yada labarai na...

KAROTA ta tabbatar da aniyarta na inganta matsayin jami’anta

Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano...

Sarkin Sanusi ya amince da nadin sabon mai unguwar Hotoro GRA

  Mai martaba Sarkin Kano na 16, Malam Muhammadu Sanusi...