Kotu ta ce Hana Muhd Sanusi II shigowa Kano ya sabawa doka

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Talatar nan, ta umurci gwamnatin jihar Kano da ta Nemi afuwar tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II a wasu jaridun kasar guda biyu.
 Kotun, a wani hukunci da mai shari’a Anwuli Chikere ya yanke, ta ce korar Sanusi daga kan karagar mulki sarautar Kano ya sabawa ka’ida, kuma ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar, kuma ya yi matukar tauye hakkinsa na dan Adam.
 Don haka, ta Umarci Gwamnatin Kanon ta baiwa Sanusin diyyar  Naira miliyan 10,
 Yayin da yake gabatar da takaitaccen bayani na karshe, lauyan Sanusi, Abubakar Mahmoud, SAN, ya shaida wa kotun cewa wanda yake karewa ba kalubalantar tsige shi.
 Mahmoud ya ce wanda yake karewa ya Kawo kara gaban kotu kan yadda ake tauye masa hakki dangane da aka yi masa bayan da gwamnatin jihar Kano ta tsige shi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...