Da dumi-dumi: Kotu Ta Rushe Shugabancin Abdullahi Abbas

Date:

Daga Munnir Muhd
 Wata babbar kotun birnin tarayya Abuja ta soke zaben Shugabannin jam’iyyar APC reshen jihar Kano da bangaren gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya gudanar a ranar Talata.
 Alkalin kotun, Mai shari’a Hamza Muazu yace ya amince da zaben da bangaren Sanata Ibrahim Shekarau suka gudanar.
 Alkalin ya yanke hukuncin cewa bangaren Shekarau mai taken G-7 ya gudanar da zaben wanda kwamitin mutane 7 na APC ya sanya wa hannu.
 POLITICS DIGEST ta ruwaito cewa wadanda suka shigar da kara sun hada da Muntaka Bala Sulaiman da mambobin jam’iyyar 17,980 yayin da wadanda ake karan su ne APC, a matsayin wanda ake kara na daya, Mai Mala Buni, shugaban riko, Sen. John Akpanudoedehe sakataren jam’iyyar na  kasa da kuma Hukumar zabe ta kasa.
 Kotun ta ce duk taron da bangaren Ibrahim Shekarau ya jagoranta sahihine.
 Nuraini Jimoh, SAN shi ne lauyan Masu Kara yayin da Sule Usman, SAN, M.N.  Duru da Mashood Alabelewe Suka kasance Lauyoyin Waɗanda ake Kara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Dangote ya rage farashin man fetur a Nigeria

Matatar mai ta dangote ta rage farashin man fetur...

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...