Karyewar Gada: Matafiya na Fuskantar Barazana a kan Iyakar Kano da Jigawa

Date:

Daga Kabir Muhd Getso
Al’umma da dama na kokawa bisa karyewar wata gada da ke iyakar Jihar kano da jigawa.
Wani matafiyi da Wakilin Kadaura24 ya zantawa da shi ya shaida masa cewar matafiya na shan bakar wahala a sakamakon lalacewar gadar, inda ta kai dole sai dai a gangara ta kasan gadar  abi ta cikin ruwa domin tsallakawa Wanda hakan kan haifar da lalecewar ababan hawa da dama.
Wasu mazauna yankin sun bayyana wahalar da matafiya ke sha a kokarin tsallaka wannan gada, sun kara da cewar tun kafin ta gagara hawa sunyi kira ga mahukunta amma ba’a samu nasarar kawo mata dauki ba. Don haka suke kira ga mahunta da su dauki kwakkwaran mataki akan wannan gada.
Shi ma shugaban karamar hukumar Birnin kudu dake Jihar Jigawa Hon Magaji Yusuf Gigo ya bayyana mana cewar duk da cewar wannan aiki na Gwamnatin tarayyar ne za su bi duk matakin da ya kamata wajen tuntubar ‘yan majalisu domin samun gudanar da wannan aiki cikin gaggawa.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...