Karyewar Gada: Matafiya na Fuskantar Barazana a kan Iyakar Kano da Jigawa

Date:

Daga Kabir Muhd Getso
Al’umma da dama na kokawa bisa karyewar wata gada da ke iyakar Jihar kano da jigawa.
Wani matafiyi da Wakilin Kadaura24 ya zantawa da shi ya shaida masa cewar matafiya na shan bakar wahala a sakamakon lalacewar gadar, inda ta kai dole sai dai a gangara ta kasan gadar  abi ta cikin ruwa domin tsallakawa Wanda hakan kan haifar da lalecewar ababan hawa da dama.
Wasu mazauna yankin sun bayyana wahalar da matafiya ke sha a kokarin tsallaka wannan gada, sun kara da cewar tun kafin ta gagara hawa sunyi kira ga mahukunta amma ba’a samu nasarar kawo mata dauki ba. Don haka suke kira ga mahunta da su dauki kwakkwaran mataki akan wannan gada.
Shi ma shugaban karamar hukumar Birnin kudu dake Jihar Jigawa Hon Magaji Yusuf Gigo ya bayyana mana cewar duk da cewar wannan aiki na Gwamnatin tarayyar ne za su bi duk matakin da ya kamata wajen tuntubar ‘yan majalisu domin samun gudanar da wannan aiki cikin gaggawa.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...