Hukuncin Kotu ya Shafi Zaben Shugabanin Mazabu ne Kawai – Muhd Garba

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Jam’iyyar APC a jihar Kano ta ce hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke a ranar Talatar da ta gabata ya shafi zabukan Shugabanin jam’iyyar APC na matakan mazabu ne kawai ba shugabannin jam’iyyar na jiha ko na kananan hukumomi ba.
 A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar, ya ce Shugabannin jam’iyyar a jihar har yanzu su hedikwatar jam’iyyar ta amince da su a Matsayin halasttun Shugabanin.
 Sai dai ya ce jam’iyyar zata saukaka  kara ne don kalubalantar hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke.
 Malam Garba ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da su kwantar da hankulansu su ci gaba da gudanar da ayyukansu kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanada.

19 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...