Hukuncin Kotu ya Shafi Zaben Shugabanin Mazabu ne Kawai – Muhd Garba

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
 Jam’iyyar APC a jihar Kano ta ce hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yanke a ranar Talatar da ta gabata ya shafi zabukan Shugabanin jam’iyyar APC na matakan mazabu ne kawai ba shugabannin jam’iyyar na jiha ko na kananan hukumomi ba.
 A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ya fitar, ya ce Shugabannin jam’iyyar a jihar har yanzu su hedikwatar jam’iyyar ta amince da su a Matsayin halasttun Shugabanin.
 Sai dai ya ce jam’iyyar zata saukaka  kara ne don kalubalantar hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke.
 Malam Garba ya yi kira ga ‘yan jam’iyyar da su kwantar da hankulansu su ci gaba da gudanar da ayyukansu kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanada.

19 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...