Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kaduna ta dage dokar dakatar da hanyoyin sadarwa a Jihar

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa
 Gwamnatin jihar Kaduna ta dage dakatarwar da ta yiwa Hanyoyin sadarwa Wanda aka dakatar na tsawon watanni uku sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga suke kaiwa Wasu sassan Jihar Kaduna.
 Gwamnatin jihar ta bakin kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan, wanda ya sanar da hakan a ranar Juma’a, ya ce an umarci hukumar da ta dace da harkokin sadarwa da ta dage dakatarwa.
Daily Trust ta ruwaito cewa, Saboda bukatar hukumomin tsaro gwamnatin jihar ta umurci hukumar sadarwa ta kasa (NCC) da ta rufe harkokin sadarwa a wasu kananan hukumomin jihar.
 Sai dai Rahotanni sun ruwaito cewa an samu karuwar ‘yan fashi da makami musamman a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a lokacin da aka dakatar da hanyoyin sadarwar.
 Aruwan ya ce sauran matakai kamar dokar hana babura, hana kasuwannin mako-mako, sayar da man fetur a cikin jarakuna na ci gaba da aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...