Gwamna Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyya ga Murtala Garo bisa Rasuwar Kanwar Mahaifinsa

Date:

Daga Khadija Abdullahi
 Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya Mika Sakon ta’aziyyarsa ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo bisa rasuwar kanwar Mahaifinsa Hajiya Hadiza Galadima Abubakar.
Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Gwamnan Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24 yace Rashin Hajiya Hadizan Babban rashi ne ga al’ummar Jihar Kano.
 Gwamna Ganduje ya bayyana cewa “Don haka ina mika wannan ta’aziyya ga kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo, da daukacin iyalanta, da al’ummar garin Garo da karamar hukumar Kabo, a madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano.
 Ya kuma addu’ar Allah ya gafarta, Sannan ya bukaci ‘yan uwa da su Kara Hakurin rashinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...