Inganta Ilimi: Mun raba kayan karatu na sama da Naira miliyan 15 a kumbotso – Garban Ƙauye

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam

 

Karamar Hukumar Kumbotso a nan kano ta tashe zunzurun kudi kusan Naira milyan 15 domin samar da kayyakin koyo da koyarwa da kuma kayan makaranta ga Daliban makarantun firaimare Guda 55 a yankin.

 

shugaban karamar Hukumar, Alhaji Hassan Garba Farawa, shine ya tabbatar da haka, yayin kaddamar da Rabon kayyakin, yana mai cewa an zabi makarantu Guda Biyar daga dukkannin mazabun karamar Hukumar ta Kumbotso, yayinda aka Raba littattafan karatu dana Rubutu da kayan makaranta ga Dalibai maza da mata domin tallafawa yunkurin Gwamnatin jiha na samar da Ilimi kyauta kuma wajibi.

Wannan na kunshe Cikin wani sako da Mai taimakamasa kan harkokin yada labarai Shazali farawa ya sanyawa Hannu.

kazalika Farawa yace yanzu haka karamar Hukumar ta sayi fili da kudinsa ya kai Naira milyan 20 inda zata kashe Naira milyan 52 wajen Gina makaranta ta zamani a yankin karamar Hukumar, Bugu da kari shugaban karamar Hukumar Alhaji Hassan Garba Farawa yace karamar Hukumar ta samar da tallafin karatu ga Dalibai domin yin karatu a jami’ar Istiqama dake Garin sumaila, awani banagare na yunkurinta wajen inganta harkokin Ilimi a jihar nan.

 

Wasu daga cikin shuwagabannin makarantun da suka amfana da Tallafin , sun yabawa yunkurin Shugaban karamar Hukumar, sun kuma bada tabbacin zasu Raba kayyakin yadda yakamata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...