Magance sheye-shaye ne kadai zai kawo karshen matsalar tsaro da talauci a Nugeria – Shugabar LESPADA

Date:

Daga Usman Usman

 

Ambassador Maryam Hassan shugabar kungiyar wayar da kan Al’umma da taimakawa wadanda suka fada shaye-shaye ta League for Societal Protection Against Drugs Abuse (LESPADA) ta ce matukar al’umma ba su tashi tsaye waje yaki dakile shada da fataucin miyagun kwayoyi a tsakanin matasa ba, zai yi wuyar a magance barazanan tsaro, talauc da jahilci .

Amb. Maryam Hassan ta bayyana hakan ne yayin wata ganawa da wakilin Kadaura24.

InShot 20250309 102512486
Talla

Ya ce suna kokari wajen bada ta wu gudunmawa a cikin wannan al’umma don Samun matasa masu kishin cigaban kasa Samar da aikinyi domin inganta Rayuwa jama’a.

Daga cikin ayyukan kungiyar ta (LESPADA) sun hada da wayar da kan Al’umma a gurare daban-daban kamar makarantu, kasuwanni da duk wani wuri na taron jama’a harma da kulawa da wadanda matsalar shaye-shaye ta shafa daga bisani a taimaka rayuwar su ta fuskar Sana’o’i da aikin yi musamman matasa.

kazalika Ambassador Maryam Hassan ta kara da cewa daga cikin abubuwan da suke sa matasa na fadawa shaye-shaye akwai sakacin da iyaye su ke yi wajan kulawa da tarbiyyar ya’yansu, da kuma rashin sauke nauyin da Allah ya dora masu na tarbiyyar da dawainiyar gida.

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Guda daga cikin masu rajin matasa sun zama matane na kwarai Comard Danmallan mai shayi bakin Abatúwa ya bayyana cewa dukkanin Al’umma sai sun taimaka wajan kulawa da tarbiyyar matasa, musamman bangaran shaye-shaye wanda yawanci shine yake tunzawa don aikata munanan ayyuka da lalata lafiya jiki dana Rohi.

Daga karshe Danmallan ya shawarci gwamnati da ta hada kai da irin wadannan kungiyoyi na inganta Rayuwa Al’umma da kuma ba su goyan bayan wajan yadda za a tsafatace jihar Kano daga Shaye-shaye wanda hakkan zai bukasa tattalin arziki da zaman lafiya a tsakanin jama’a.​

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...