Kungiyar Daneji Amintacciya ta karrama Wasu Masu tallafawa Ilimi a Kano

Date:

Daga Kamal Yakubu Ali

 

shugaban kungiyar Daneji Amintacciyya Alhaji Salisu Mai Manja ya bayyana ingantaccen Ilimi da Cewa shi ne hanya daya tilo da za’a bi domin Magance Matsalolin da al’umma suke fuskanta.
Alhaji Salisu Mai Manja ya bayyana hakan ne yayin bikin karrama wasu manya mutane wadanda suke bada gudunmawa wajan bunkasa harkokin ilimi da rayuwar al’ummar dake yankin unguwannin marmara Daneji, kwalwa da mandawari.
Alh salisu mai manja yace ya zama wajibi ga iyaye su hada hannu da masu kishi dake cikin al’umma domin samarda ingantaccen ilimi ga ‘ya’yansu.
Anasa jawabin shugaban kungiyar alkalami yafi takobi  Malam Nazir Musa Shehu yace sun zabo Mutanen da suka karrama ne duba irin gudunmawar da suke bayarwa wajan tallafawa masu karamin karfi dake cikin al’umma .
Mutanen  aka karrama sun hadarda Malam Abdullah Daneji, Alh Muntari na Wali, Alh Hamisu Jingau Sai masu Unguwanin Marmara, kwalwa, Mandawari da kuma Daneji.
 Wakilin Kadaura24 Kamal yakubu Ali ya bamu labarin cewa taron ya samu halarta al’umma da dama a fadin Jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Magance sheye-shaye ne kadai zai kawo karshen matsalar tsaro da talauci a Nugeria – Shugabar LESPADA

Daga Usman Usman   Ambassador Maryam Hassan shugabar kungiyar wayar da...

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...