Har yanzu jam’iyyar APC ta kasa bata tabbatar da waye shugaban ta ba a Kano – Isma’il Ahmad

Date:

 

Guda daga cikin ‘yan kwamatin riko na uwar jam’iyyar APC ta kasa, kuma shugaban matasa na kasa Isma’il Ahmad ya bayyana cewar har yanzu uwar jam’iyyar APC ta kasa bata kai ga ayyana waye sahihin shugaban jam’iyyar a Kano ba.

 

Isma’il Ahmad ya bayyana hakan ne a Wata Zantawa da sukai da  gidan Rediyo Freedom dake Kano, inda yace uwar jam’iyyar zata yi nazari sannan ta fadi matsayarta akan shugabancin jam’iyyar reshen jihar Kano.

 

A karshen makon jiya ne dai aka samu bangarori guda biyu masu hamayya da juna na ikirarin sune halastattun shugabannin jam’iyyar bayan da kowanne yake ikirarin an zabe shi tsakanin bangaren Abdullahi Abbas dake tare da Gwamnatin Kano, da kuma bangaren Danzago da suke tare da Sanata Ibrahim Shekarau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...