Har yanzu jam’iyyar APC ta kasa bata tabbatar da waye shugaban ta ba a Kano – Isma’il Ahmad

Date:

 

Guda daga cikin ‘yan kwamatin riko na uwar jam’iyyar APC ta kasa, kuma shugaban matasa na kasa Isma’il Ahmad ya bayyana cewar har yanzu uwar jam’iyyar APC ta kasa bata kai ga ayyana waye sahihin shugaban jam’iyyar a Kano ba.

 

Isma’il Ahmad ya bayyana hakan ne a Wata Zantawa da sukai da  gidan Rediyo Freedom dake Kano, inda yace uwar jam’iyyar zata yi nazari sannan ta fadi matsayarta akan shugabancin jam’iyyar reshen jihar Kano.

 

A karshen makon jiya ne dai aka samu bangarori guda biyu masu hamayya da juna na ikirarin sune halastattun shugabannin jam’iyyar bayan da kowanne yake ikirarin an zabe shi tsakanin bangaren Abdullahi Abbas dake tare da Gwamnatin Kano, da kuma bangaren Danzago da suke tare da Sanata Ibrahim Shekarau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...