Majalisa ta hana Ganduje Gina shaguna a masallacin fagge

Date:

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta umarci gwamnatin jihar da ta dakatar da gina shagunan kasuwanci a Masallacin Juma’a na Fagge da ke kwaryar birnin jihar.

Kakakin Majalisa Hamisu Ibrahim Chidari ne ya bayar da umarnin yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya ce sun kafa kwamati domin bincike kan shagunan da ake ginawa.

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisa Abdu Madari ya faɗa wa BBC Hausa cewa sun ɗauki matakin ne biyo bayan zargin da ake yi na almundahanar kuɗi.

“A matsayinmu na ‘yan majalisa mun dakatar da ginawa ko kuma sayar da wani fili daga cikin farfajiyar Masallacin Juma’a na Fagge har sai mun kammala bincike,” a cewar shugaban masu rinjayen.

Dan majalisa mai wakiltar karamar Hukumar Bunkure, Muhammad Uba Gurjiya, shi ne zai jagoranci kwamatin na mutum takwas, wanda ake sa ran zai gabatar da rahotonsa cikin mako biyu.

Lamarin na faruwa ne kwana daya bayan Sheikh Tijjani Bala Kalarawi ya sauka daga muƙaminsa a kwamatin Masallacin Fagge saboda zargin badaƙalar da ke cikin aikin gina shagunan.

A baya-bayan nan gwamnatin Kano karkashin jagorancin Abdullahi Umar Ganduje na gina sabbin shagunan kasuwanci a wurare daban-daban da ke tsakiyar birnin Kano, abin da ke jawo cecekuce tsakanin jama’ar gari.

26 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...