Zamu sa kafar Wanda guda da Masu Sayar da Jabun Kaya a Kano – Gen. Dambazau

Date:

Daga Halima M Abubakar

Hukumar Kare hakki Masu Siya da Masu sayarwa ta jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar kare masu siyayya ta hanyar rage yaduwar jabun kayayyakin da wa’adin su ya kare.

Kadaura24 ta rawaito Sabon Manajan Darakta na Hukumar Birgediya Janar Idris Dambazau RTD ne ya bayyana hakan a lokacin da yake Zantawa da Manema labarai a kano.

Ya ce Hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kama duk wadanda ke harkar sayar da kayayyakin da wa’adin suka kare da Kuma na jabu.

Idris Dambazau ya bayyana cewa a lokacin da ya zama sabon Manajan Daraktan hukumar, ya zo da Tsare-tsaren da suka dace don magance matsalar.

Manajan Daraktan yace wadanda ke aikata irin wannan munanan ayyukan su sani ba su da mafaka a jihar Kano, yana mai cewa ma’aikatan sa sun dukufa wajen tabbatar da an kamo wadanda suka aikata wannan aika -aika don gurfanar da su a gaban kuliya.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...