Zamu sa kafar Wanda guda da Masu Sayar da Jabun Kaya a Kano – Gen. Dambazau

Date:

Daga Halima M Abubakar

Hukumar Kare hakki Masu Siya da Masu sayarwa ta jihar Kano ta ce ta kuduri aniyar kare masu siyayya ta hanyar rage yaduwar jabun kayayyakin da wa’adin su ya kare.

Kadaura24 ta rawaito Sabon Manajan Darakta na Hukumar Birgediya Janar Idris Dambazau RTD ne ya bayyana hakan a lokacin da yake Zantawa da Manema labarai a kano.

Ya ce Hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kama duk wadanda ke harkar sayar da kayayyakin da wa’adin suka kare da Kuma na jabu.

Idris Dambazau ya bayyana cewa a lokacin da ya zama sabon Manajan Daraktan hukumar, ya zo da Tsare-tsaren da suka dace don magance matsalar.

Manajan Daraktan yace wadanda ke aikata irin wannan munanan ayyukan su sani ba su da mafaka a jihar Kano, yana mai cewa ma’aikatan sa sun dukufa wajen tabbatar da an kamo wadanda suka aikata wannan aika -aika don gurfanar da su a gaban kuliya.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...