Kwankwaso ya Fadi yadda Suka hadu da Ganduje a filin Jirgin Sama

Date:

A karon farko, tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana yadda haɗuwarsa ta kasance da abokin takun saƙarsa na siyasa, gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje a filin jirgin saman Abuja, babban birnin Najeriya.

Sanata Kwankwaso ya shaida wa BBC Hausa cewa ya riga Gwamna Ganduje zuwa filin jirgin da kamar awa guda, a lokacin ne ya samu labarin cewa shi ma magajin nasa na kan hanyar isowa filin jirgin.

“Na ce to Allah ya kawo shi, kasuwa ce ai kamar tasha ce, ba wanda za ka ce ya zo ko kar ya zo, muka shiga jirgi daya da shi muka taho, muka sauka a wanan tasha ta Kano, na kama hanyata ya kama tasa ya tafi gida.”

Rabiu Musa Kwankwaso ya ce ”A matsayi irin na Musulunci ai ba lallai sai kana jam’iyya daya da mutum za ka gaisa da shi ba, mun gaisa da shi kowa ya koma ya zauna a kujerarsa, don haka haka muka isa har Kano kowa na zaune a kujerarsa.

Kadaura24 ta rawaito tun Bayan da aka Sami sabani tsakanin Kwankwaso da Ganduje Wannan ne karon Farko da Suka gaisa da juna ,duk da abaya sun gadu a wuraren taro Amma kowa bai gaisa da Dan uwansa ba.

79 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...

Yanzu-yanzu: Manjo Hamza Al-Mustapha ya koma jam’iyyar SDP

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Major Dr. Hamza Al-Mustapha ya shiga...

Inganta aiyukan hukumar zakka hanya ce da gwamnatin za ta bi don rage talauci a Kano – Sarkin Rano

Daga Kamal Yakubu Ali   Mai martaba sarkin Rano Amb. Muhammad...