Zargin batanci : Kotu ta bada Umarnin a duba kwakwalwar Abduljabar a asibitin Dawanau

Date:

Kotun Shari’ar Musulunci dake Zamanta a Kofar kudu karkashin jagorancin Mai shari’a Malam Ibrahim Sarki Yola ta bada Umarnin Kai sheikh Abduljabar Kabara asibitin Dawanau domin duba Lafiyar kwakwalwarsa.

Yayin Zaman kotun na Wannan Rana Bayan kotun da bada Umarnin a karatowar Abduljabar laifukan da ake tuhumarsa ,Amma Abduljabar da lauyoyinsa basu ce komai ba game da tuhumar.

Kadaura24 ta rawaito Mai shari’a Ibrahim Sarki Yola ya bada Umarnin a rubuta kwafin shari’ar Baki daya a baiwa lauyoyin Abduljabar din nan take ba tare da bata Lokaci ba.

Mai shari’a Sarki Yola yace Koda lauyoyin Abduljabar sun ɗaukaka Kara hakan bazai hana cigaba da shari’ar ba.

Saraki Yola ya dage Zaman zuwa Ranar 19 ga Wannan Wata na satumba da muke ciki domin cigaba da shari’ar

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...