Da dumi-dumi: Ganduje ya aiyana Ranar Litinin mai Zuma Matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Nasiru Abubakar

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya ayyana Litinin, 1 ga Muharram, 1443 AH (9 ga Satumba, 2021) a matsayin Ranar hutun sabuwar Shekarar Musulunci a jihar.

Sanarwar da kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba ya sanya wa hannu ta bayyana cewa hutun ya kasance ne don tunawa da sabuwar kalandar Musulunci ta 1443 AH.

Gwamnan ya bukaci ma’aikata da su yi amfani da ranar don yin addu’a ga jihar Kano da kasa don kubutar da ita daga matsalolin tsaro.

Gwamna Ganduje ya kuma taya Musulmai murnar shigowar sabuwar shekarar Musulunci, wacce ke bukatar nuna godiya ga Allah .

Sanarwar ta kara neman goyan baya da hadin kai na jama’a ga gwamnati yayin da take yin bakin kokarinta don inganta kudirinsu yayin da kasar ke fuskanta kalubalen tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...