Da dumi-dumi: Ganduje ya aiyana Ranar Litinin mai Zuma Matsayin Ranar hutu

Date:

Daga Nasiru Abubakar

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya ayyana Litinin, 1 ga Muharram, 1443 AH (9 ga Satumba, 2021) a matsayin Ranar hutun sabuwar Shekarar Musulunci a jihar.

Sanarwar da kwamishinan yada labarai, Malam Muhammad Garba ya sanya wa hannu ta bayyana cewa hutun ya kasance ne don tunawa da sabuwar kalandar Musulunci ta 1443 AH.

Gwamnan ya bukaci ma’aikata da su yi amfani da ranar don yin addu’a ga jihar Kano da kasa don kubutar da ita daga matsalolin tsaro.

Gwamna Ganduje ya kuma taya Musulmai murnar shigowar sabuwar shekarar Musulunci, wacce ke bukatar nuna godiya ga Allah .

Sanarwar ta kara neman goyan baya da hadin kai na jama’a ga gwamnati yayin da take yin bakin kokarinta don inganta kudirinsu yayin da kasar ke fuskanta kalubalen tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...