Gwamna Ganduje yace ya kadu sosai da mutuwar Col. Dominic Oneya

Date:

Daga Sa’eeda Ahmad Sagagi

Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana kaduwarsa kan rasuwar tsohon Gwamnan Kano Zamani mulkin Sojoji, Kanal Dominic Obukadata Oneya, wanda ya rasu a yau, Alhamis.

Wannan na kunshe ne Cikin Wata sanarwa da Babban Sakataren yada labaran Gwamnan Kano Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24.

“A lokacin da yake Gwamnan Kano na Soja , Kanal Dominic Oneya ya yi iyakar ƙoƙarinsa wajen ciyar da jihar gaba,” in ji Ganduje.

Ganduje yace Oneya Yana da hangen nesa wajen gane abun da al’umma suke bukata Wanda Zai Kawo cigaba a Lokacinsa.

” A matsayina na Kwamishinan Ayyuka, Gidaje da Sufuri a ƙarƙashinsa, na san yadda yake da kishin ƙasa. Da gaske mun rasa dan kasa mai kishin kasa, ”in ji gwamna Ganduje.

Gwamna Ganduje ya nemi iyalan Marigayin da su yi koyi da kyawawan halayen mahaifinsu. Wanda ya jajirce wajen cigaban kasa kuma jagora mai kishin kasa.

“Har yanzu Kano tana amfana daga ginshiƙan tushe na marigayin ya kafa wa jihar abubuwa masu kyau, waɗanda wasu gwamnatoci suka kwafa daga baya,” in ji shi.

Ya yi fatan Iyalan Mamacin za su sami karfin gwiwa don jure rashin.

74 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...